Gwamnatin Mali da kuma Azbinawa ‘yan tawaye, sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu, bayan share tsawon kwanaki suna tattaunawa a birnin Ouagadougou na kasar Burkina Faso.
Shugaban kasar Iran mai jiran gado, Hassan Rohani yace gwamnatin shi ba za ta dakatar da shirin Iran na sarrafa sinadarin Nukiliya ba, duk da takunkumin da Majalisar Dinkin Duniya ta kakaba kasar a baya. Rohani mai sassaucin ra’ayi ya yi alkawarin tattaunawa da kasashen duniya kan batun ba tare da rufa rufa ba. Malam Hafiz Muhammad da ke karatu a jami’ar birnin Qum a kasar ta Iran, ya yi wa Nasirudden karin bayani kan kalaman na Sheik Rohani.